in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata mata su shiga harkokin bunkasuwar tattalin arzikin teku, in ji shugabar AU
2016-10-15 13:15:51 cri
Jiya Jumma'a, shugabar kungiyar tarayyar Afirka AU Nkosazana Dlamini Zuma ta bayyana cewa, ana bukatar halartar mata cikin bayanan kundin tsarin Lome da za a kulla, domin kyautata kundin bisa fannin gaggauta bunkasuwar tattalin arziki ta hanyoyin teku.

A yayin taron karawa juna sani na mata kan harkokin tattalin arzikin teku a lokacin taron koli na musamman kan harkokin tsaron teku na kungiyar tarayyar kasashen Afirka da aka yi a jiya Jumma'a, Madam Zuma ta bayyana cewa, ana fatan shigar da mata cikin aikin neman bunkasuwar tattalin arziki na teku, saboda lamari ne da zai baiwa mata 'yanci da kuma dogaro da kansu, inda za su sami ayyukan yi, da kafa kamfanoni na kashin kansu, ta yadda za su bada gudummawa wajen raya tattalin arzikin nahiyar Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China