in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sake maido da birnin Aleppo a karkashin mallakar gwamnatin kasa yana da muhimmiyar ma'ana, in ji shugaban Syria
2016-12-08 13:27:29 cri
Jiya Laraba, shugaban kasar Syria Bachar al Assad ya bayyana cewa, sake maido da birinin Aleppo dake arewacin kasar a karkashin mallakar gwamnatin kasar Syria yana da muhimmiyar ma'ana ta fannin soja da siyasa ga gwamnatin kasar.

Haka kuma, shugaba Assad ya ce, tun da farko gwamnatin kasar Syria ta tsai da kudurin 'yantar da yankin Aleppo, sabo da birnin ya kasance muhimmin birni kamar babban birnin kasar Damascus yake a duk fadin kasar ta fannin siyasa da tattalin arziki.

Bugu da kari, rundunar sojan kasar ta bayyana a ran 7 ga wata cewa, sojojin gwamnatin kasar sun kwace tsohon yankin birnin Aleppo gaba daya sakamakon matakan sojan da suka dauka a wannan rana.

Dangane da wannan lamari, kungiyar sa ido kan yanayin hakkin dan Adam wadda hedkwatarta dake birnin London na kasar Burtaniya ta bayyana cewa, dakarun kungiyar adawa da gwamnati sun fara janye jikinsu daga tsohon yankin birnin Aleppo zuwa kudancin birnin, hakan ya sa, gwamnatin kasar Syria ta kwace kashi 8 bisa 10 na yankin dake hannun dakarun adawa a birnin Aleppo. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China