in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Syria ta ki yarda da kudurin OPCW
2016-11-14 10:27:49 cri
Ma'aikatar harkokin waje ta kasar Syria ta bayar da sanarwa a jiya Lahadi, wadda ke nuni da kin yarda da kudurin hukumar haramta makamai masu guba, wato OPCW, wanda ya tabbatar da bukatar binciken na'urorin soja da kuma hukumomin kasar ta Syria.

Cikin kudurin hukumar haramta makamai masu guba da aka zartas a ranar 11 ga wata, an zargi sojojin gwamnatin Syria, da kuma kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta IS da yin amfani da makamai masu guba a kasar Syria, kudurin ya kuma nuna goyon baya ga gudanar da bincike a kan na'urorin soja, da kuma hukumomin nazari a cikin kasar Syria.

Game da hakan, ma'aikatar harkokin waje ta Syria ta nuna rashin yarda da wannan zargi, kuma a cewarta, ana nuna mata bambanci ne kawai.

Sanarwar ta ce, wasu kasashe sun mai da hukumar haramta makamai masu guba a matsayin abin da zai taimaka musu cimma burinsu na siyasa. Yanzu haka dai gwamnatin Syria tana tantance kudurin, kuma nan ba da jimawa ba, za ta fitar da takarda a hukunce don bayyana matsayinta.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China