in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta jefa kuri'ar kin amincewa da wani daftari game da Syria
2016-12-07 20:39:50 cri
A jiya Talata ne kwamitin Sulhun MDD ya kira wani taro, inda mambobinsa suka jefa kuri'a kan wani daftarin shirin da wasu kasashen da suka hada da Masar, da Spaniya, da New Zealand suka mika ma kwamitin, dangane da maganar Syria. A yayin taron, wasu mambobin kwamitin sulhun, ciki har da kasar Sin, sun jefa kuri'ar kin amincewa da wannan daftari. Dagane da batun, mista Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya ce kasar Sin ta jefa kuri'ar ce bisa la'akari da matsayin da kasar Sin ta dade tana tsayawa a kai, dangane da batun Syria.

A cewar jami'in kasar Sin, yanzu haka yanayin da ake ciki a kasar Syria yana da sarkakiya matuka. Saboda haka, kamata ya yi, kwamitin sulhu na MDD ya yi kokarin ganin bangarori daban daban sun cimma ra'ayi daya, tare da kiyaye hadin kan mambobin kwamitin, ta yadda za a samu damar taimakawa kokarin warware maganar Syria ta hanyar lumana. A sabili da haka, kasar Sin ta ki yarda da yadda aka nemi zartas da wani shirin da ake da sabanin ra'ayi a kansa. Dabarar da wasu kasashen suka bullo da ita ta tilastawa mambobin kwamitin sulhu zartas da wani kuduri ba za ta taba yin amfani ba, sai dai ta jawo baraka ga kwamitin, in ji jami'in kasar Sin.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China