in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Libya sun mamaye birnin Sirte
2016-12-06 10:35:15 cri
A jiya Litinin 5 ga wata, gwamnatin hadin kan al'ummar Libya ta sanar da cewa, sojoji masu tsaron gwamnati sun riga sun kawar da dakarun kungiyar IS daga birnin Sirte, har ma sun karbe birnin baki daya.

Tun daga watan Mayu zuwa yanzu, gwamnatin Libya ta kafa rundunar soja mai tsaron gwamnati domin kai samame kan birnin Sirte dake hannun kungiyar IS, tare da mamaye mafi yawansa a cikin gajeren lokaci. Amma a kan wasu tituna, rarar dakarun kungiyar IS su kan mai da martani tare da gwanayen harbe da kai harin kunar bakin wake da motocin da aka dasa boma-bomai. A sabili da haka, an shiga halin kiki-kaka.

A shekarar 2011, bayan kifar da mulkin Muammar Gaddafi, kasar ta fada cikin yakin basasa. Kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi da na ta'addanci sun kara karfinsu a kasar a daidai wannan lokaci. A cikin wannan yanayi kuma, kungiyar IS ta mamaye biranen Sirte, Derna da sauransu, tare da kafa sansanoni a kusa da biranen Tripoli, Benghazi da dai sauransu. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China