in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta kaddamar da hare hare ta sama kan IS bayan da gwamnatin Libya ta bukaci hakan
2016-08-02 10:34:56 cri
A jiya Litinin ma'aikatar tsaro ta Pentagon ta ce Amurka ta kaddamar da hare hare ta sama kan kungiyar IS a Libya kamar yadda gwamnatin kasar Libyan ta bukata.

Koda yake, wannan ba shine karon farko da Amurkar ta kaddamar da hare hare kan mayakan IS a Libya ba, sai dai wannan shine karon farko da gwamnatin hadakar Libyan ta bukaci Amurkar ta kaddamar da hare haren ta jiragen sama a hukumance. A cewar mai Magana da yawun ma'aikatar tsaro ta Pentagon Peter Cook, Amurkar ta kaddamar da hare haren ne a Sirte, wani birnin dake yankin tekun Mediteraniya, bayan da shugaba Barack Obama ya bada umarni.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China