in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin Libya sun ceto mutane 13 da IS ta yi garkuwa da su
2016-10-23 13:08:01 cri
Jiya Asabar, sojojin tsaro na gwamnatin hadin kan al'ummar kasar Libya sun ceto mutanen kasashen ketare 13 da aka yi garkuwa da su bayan wani kazamin fada da dakarun kungiyar IS a birnin Sirte dake yammacin kasar.

An samu labarin daga kakakin watsa labaru na gwamnatin hadin kan al'ummar kasar cewa, bayan kazamin yaki na kwanaki uku a tsakanin sojojin tsaron gwamnatin da dakaru masu tsattsauran ra'ayi, an cimma nasarar kwato yawancin birnin dake hannun kungiyar IS, kuma aka ceto wadannan mutane 13, ciki har da 'yan kasar Eritoria 11, 'dan kasar Turkiya 1 da kuma 'dan kasar Masar 1.

A shekarun nan, kungiyoyin ta'addanci da na masu tsattsauran ra'ayi suna amfani da yanayin tashe-tashen hankula a kasar Libya don habaka karfinsu a kasar. Tun daga watan Mayu na bana, gwamnatin hadin kan al'ummar Libya ta kafa kawancen sojojin sa kai dake yaki da kungiyar IS, don kara murkushe dakarun IS dake Sirte da sauran yankuna, kuma a watan Agusta ne ta sanar da cewa, an samu babban ci gaba kan matakan soja da suka dauka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China