in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi jigilar makamai masu guba zangon karshe daga kasar Libya
2016-08-31 13:43:16 cri
Wani jami'in gwamnatin hadin gwiwar al'ummar kasar Libya, ya bayyana a jiya Talata cewa, bisa taimakon jiragen ruwa na kasar Denmark, an yi jigilar makamai masu guba zangon karshe, daga mashigin teku na Misratah na kasar Libya zuwa kasar Jamus don lalata su.

Mataimakin firaministan gwamnatin kasar Moussa al-Koni, ya bayyana cewa, an riga an kai dukkan makamai masu guba na kasar zuwa kasashen waje don lalata su.

Majalisar dokokin kasar Denmark ta jefa kuri'a a ranar 19 ga wannan watan nan, inda aka amince da gwamnatin kasar ta tura jiragen ruwa don halartar aikin jigilar makamai masu guba, daga kasar Libya zuwa kasashen waje. Game da hakan ministan harkokin wajen kasar Denmark Kristian Jensen, ya bayyana cewa an gudanar da jigilar makaman zangon karshe ne, don hana fadawar su hannun kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China