in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya nuna yabo kan sabon kudurin da kwamitin sulhu ya zartas kan Koriya ta Arewa
2016-12-01 11:02:31 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon a ranar Laraba ya nuna yabo kan yadda aka zartas da wani sabon kuduri a kwamitin sulhu na majalisar don mayar da martani ga gwajin makaman nukiliya da kasar DPRK wato Koriya ta Arewa ta yi a ranar 9 ga watan Satumban bana, haka zalika ya bukaci dukkan mambobin majalisar da su yi iyakacin kokari don tabbatar da aiwatar da kudurin yadda ya kamata.

Cikin sakonsa, mista Ban ya ce yana farin ciki ganin yadda aka zartas da kudurin ba tare da samun sabanin ra'ayi ba. A cewarsa, yadda aka zama tsintsiya madaurinki daya a wannan karo zai taka muhimmiyar rawa wajen daidaita al'amura a zirin Koriya, gami da sauran sassan duniya.

Ya fara daga watan Janairun bana, kasar Koriya ta Arewa ta yi gwajin makaman nukiliyarta har sau 2, gami da gwajin makamai masu linzami a kalla har sau 25. Irin yanayin da kasar take ciki ya sa kwamitin sulhu na MDD ya kira taron gaggawa karo na 9 cikin wannan shekara, don samar da dabarar da za a dauka ta yadda za a kau da matsalar nukiliya a zirin Koriya. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China