in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta shirya bikin tunawa da 'ranar nuna goyon baya da Jama'ar Falasdinu'
2016-11-30 11:34:48 cri
Jiya Talata, a hedkwatar MDD dake birnin New York na kasar Amurka, an shirya biki don tunawa da ranar musamman ta 'Nuna ma Jama'ar Falasidinu goyon baya', inda masu halartar biki na bangarori daban daban suka yi kira ga Isra'ila da Falasdinu da su yi kokarin shimfida imani tsakaninsu, gami da sake bude shawarwari.

Babban sakataren Majalisar Ban Ki-moon ya yi jawabi wajen bikin cewa, rikici tsakanin Isra'ila da Falasdinu tamkar wani gyambo ne wanda ya dade ya ki warkewa, tare da sanadiyyar dauki-ba-dadi a daukacin zirin gabas ta tsakiya. A shekarun baya, shawarwari karo 2 da Isra'ila da Falasdinu suka yi duk sun yi zub da ciki, har ma an samu abkuwar fadace-fadace yayin shawarwarin, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane fiye da dubu 1, galibinsu fararen hula 'yan Falasdinu.

A cewar Ban Ki-moon, za a shiga shekara ta 50 ne bayan da bangaren Isra'ila ya mamaye harabar Falasdinu, amma har zuwa yanzu an kasa ganin alamar cimma daidaito tsakanin bangarorin 2. A yanzu haka, kamata ya yi, gamayyar kasa da kasa su bayyana niyyarsu ta taimakawa bangarorin Isra'ila da Falasdinu don su sake shimfida imani tsakaninsu, da samar da damar gudanar da shawarwari.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China