Shugaban majalisar dattawan Najeriya Bukoka Saraki ya bayyana a jiya Alhamis ce, majalisar tana fatan kammala gyaran kudin tsarin mulkin kasar zuwa watan Janairun shekara mai zuwa.(Daliy Trust)
A wani labarin kuma majalisar dattawan Najeriyar ta ce, ta gaji yadda ake kirkiro dokoki ba tare da ganin ana aiwartar da su yadda ya kamata ba. A saboda haka shugaban majalisar dattawan ya jaddada bukatar hada kirfi da karfe wajen ganin an kawo karshen wannan lamari.(Vanguard)
Asusun kudaden ajiyar ketare na Najeriya ya karu da dala miliyan 589 a 'yan makonnin da suka gabata, duk da bukatar da ake da ita.
Yanzu haka akwai kudade da yawansu ya kai dala biliyan 24.49, sabanin dala biliyan 23.91 da ke cikin asusun a makonnin hudun da suka gaba, adadin dake wakiltar karuwar kashi 2.5 cikin 100.(The Guardian)