in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'i: Danyen man Najeriya yana da farin jini a kasuwanni
2016-11-25 09:34:13 cri
Wani kusa a gwamnatin Najeriya ya ce danyen man kasar yana da matukar farin jini a kasuwannin duniya.

Maikanti Baru, shi ne manajan daraktan kamfanin mai na kasar NNPC, ya tabbatar da hakan ga 'yan jaridu a Abuja, bayan kaddamar da tallar kwangilar aikin hako man kasar na shekarar 2016/2017.

Ya ce albarkatun man Najeriyar ba abin yarwa ba ne, kuma yana matukar jan hankullan 'yan kasuwar dake aikin tace danyen mai, saboda kyakkyawan yanayin da man yake da shi.

Baru, ya kara da cewa, akwai abubuwa masu daraja da ake fitarwa daga danyen man kasar, hakan ne ya sa yake da farin jini a kasuwannin duniya.

Najeriya tana hako gangar danyen mai dubu 600 ne a kullum tun bayan hare haren farfasa bututun man kasar lamarin da ke haifar da tafiyar hawainiya wajen hako danyen man kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China