Babban sifeton 'yan sandan Najeriya Ibrahim Idris, ya ce kimanin 'yan sandan kasar 128 ne aka hallaka a lokacin da suke bakin aiki cikin watanni 3 da suka gabata.
Jami'in ya ce 'yan sandan sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da suke kokarin dakile hare hare da kuma tabbatar da bin doka da oda a sassan kasar dabam dabam.
Cikin wata sanarwa da ta iske kamfanin dillanci labarai na Xinhua, sifeton 'yan sandan ya ce, wasu daga cikin jami'an nasu sun mutu ne a lokacin da wasu 'yan bindiga suka afkawa wasu yankunan jihar Zamfara a shiyyar arewa maso yammacin kasar, da jihar Anambara da ke kudu maso gabashin kasar, da kuma dakile barnar tsagerun Niger Delta a gabar teku na Okrika dake jihar Rivers mai arzikin mai.
Ya ce ana cigaba da daukar matakai domin kawo karshen hallaka jami'an 'yan sandan Najeriyar.(Ahmad Fagam)