in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya taya murnar cika shekaru 50 da kafuwar UNIDO
2016-11-21 20:50:10 cri

A yau Litinin ne, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya aika wasikar taya murnar cika shekaru 50 da kafa kungiyar raya masana'antu ta MDD wato UNIDO.

A cikin wasikar, Li Keqiang ya ce, kasar Sin tana kira ga kasashen duniya da su kara yin hadin gwiwa a fannin sarrafa kayayyaki, a kokarin ganin sun taimakawa juna domin samun moriyar juna da nasara tare, tare da lalubo bakin zaren inganta sabuwar hanyar hada kan kasashe maso tasowa da kuma hada kan kasashe maso tasowa da masu ci gaba.

Firaministan kasar Sin ya kara da cewa, a matsayinta na kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin za ta ci gaba da mara wa kungiyar UNIDO baya. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China