in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya ta bunkaci kamfanoni kasa da kasa da su taimaka mata wajen bunkasa sashen kiwon kifin kasar
2016-11-11 09:27:04 cri

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi kira ga kamfanonin kasa da kasa da ke da alaka da aikin gona, da su agazawa sashen kiwon kifin kasar.

Darektan sashen kiwon kifi na kasar Mu'azu Mohammed shi ne ya yi wannan kiran yayin wani taron kara wa juna sani da aka shirya a Abuja, fadar mulkin kasar.

Ya ce, muddin irin wadannan kamfanoni suka taimaka da kayayyakin noma na zamani, samar da horo ga masu kiwon kifi da samar da abincin kifaye masu inganci, hakan zai taimaka wajen samar da isassun kifaye, zai kuma rage kiyafen da ake shigo da su cikin kasar.

Darektan ya kuma yi kira ga kasashen duniya da su kawo dauki a bangaren bincike, game da abin da ya kira abincin kifaye marasa inganci da ake samarwa a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China