in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An damke mutane 16 da suka buya a jirgin ruwa a kokarin zuwa Amurka
2016-11-07 09:46:19 cri
Hukumar tsaron jiragen ruwa ta Najeriya(NIMASA) gami da sojojin ruwan kasar, sun kama mutane a kalla 16 da suka buya a cikin wani jirgin ruwa da ke shirin zuwa Amurka.

Kakakin hukumar ta NIMASA Lami Tumaka ta bayyana a cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin kasar Sin na Xinhua ya samu kwafe cewa,an gudanar da kamen ne a ranar Jumma'a kusa da gabar ruwan Legas.

A cewarta, binciken farko-farko ya nuna cewa, mutanen masu kutse ne kawai da suka so bin jirgin zuwa kasar Amurka domin samun rayuwa mai inganci a can.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China