in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta fara bincike game da zargin yiwa mata fyade a sansanin 'yan gudun hijira
2016-11-08 09:48:46 cri
Gwamnatin Najeriya ta fara gudanar da bincike game da zargin da ake yi wa wasu jami'an sojoji da 'yan sanda kasar na yiwa wasu mata da 'yan mata fyade a sansanonin 'yan gudun hijira.

A ranar Litinin da ta gabata ne, hukumar 'yan sandan Najeriya ta sanar da cewa, ta tura 'yan sanda mata kimanin 100 zuwa sansanonin 'yan gudun hijirar, domin su gudanar da bincike. Manufar tura jami'an shi ne, domin tabbatar da tsaron lafiyar dubban mata da kananan yara dake rayuwa a sansanonin.

A makon jiya ne, shugaban Najeriya Muhammad Buhari ya bada umarnin a gaggauta gudanar da bincike, bayan samun wani rahoto da hukumar kare hakkin dan adama ta fitar, inda ya zargi wasu daga cikin sojoji da 'yan sandan kasar da aikata fyade kan mazauna sansanonin 'yan gudun hijira a kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China