in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Najeriya yawan fasa bututun man kasar ya ragu
2016-11-04 09:58:53 cri
Hukumar kula da albarkatun man fetur ta Najeriya NNPC, ta sanar a jiya Alhamis cewa, matsalar farfasa bututan mai da ake fama da shi a kasar ya ragu da kaso 28.94 cikin 100, sakamakon yunkurin da gwamnatin tarayya ke yi a kwanan nan na kawo dauki don dakile matsalar yawaitar farfasa bututan man, wanda tsagerin yankin Niger Delta ke kaddamarwa a yankin mai arzikin mai.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na internet, hukumar ta NNPC ta ce, tun daga watan Augusta yawan farsata bututun man kasar ya fara raguwa, idan aka kwatanta wanda aka samu a watan Yuli wanda ya kai kimanin 311.

A halin yanzu, gwamnatin Najeriya tana cigaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki a yankin Niger Delta, domin lalibo bakin zaren cimma yarjejeniyar sulhu da tsagerun yankin don kawo karshen ta'annatin da suke yiwa kayayyakin aikin hakon danyen man kasar.

Ganawa ta baya bayan nan ita ce wanda shugaba Muhammadu Buhari da kansa ya jagoranta, wacce aka fara a ranar Litinin din da ta gabata, tare da shugabannin yankin Niger Delta inda suka gabatar da bukatunsu ga shugaban kasar, wanda suke ganin biyan bukatun zai samar da dawwammman zaman lafiya a yankin.

Matsalar yawaitar farfasa bututan man a yankin, ta haddasa raguwar adadin danyen man da kasar ke samarwa.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China