in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a bi ka'idoji guda uku a yayin shawarwarin babban taron yanayi na Marrakech, in ji wakilin Sin
2016-11-10 09:40:42 cri
Mataimakin shugaban tawagar wakilan kasar Sin a babban taro karo na 22 na kasashen da suka kulla yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD da ake yi a birnin Marrakech na kasar Morocco, kana manzon musamman game da shawarwari kan harkokin sauyin yanayi na ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Gou Haibo ya bayyana cewa, ya kamata a bi ka'idoji guda uku a yayin da ake gudanar da taron birnin Marrakech.

Wadannan ka'idoji uku sun hada da, na farko, ya kamata a daidaita ayyukan da ake yi a fannonin magance matsalar sauyin yanayi da neman fasahohin da abin ya shafa da kuma neman taimakon kudade game da wannan aiki da sauransu a yayin da ake aiwatar da yarjejeniyar Paris. Na biyu, bai kamata a yi watsi da ra'ayin da aka cimma ba. Na uku kuma na karshe, ya kamata a fahimtar da kasashe masu tasowa game da wannan aiki, yayin da ake kokarin taimakawa gwamnatocin kasashen duniya yadda za su karfafa wannan aiki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China