in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe 100 sun sanya hannu kan yarjejeyar Paris
2016-11-07 09:00:56 cri
Babbar sakatariyar kula da taron sauyin yanayi na MDD(UNFCCC) Patricia Espinosa ta bayyana a jiya Lahadi cewa, ya zuwa yanzu kasashe 100 ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta birnin Paris.

Jami'ar ta sanar da hakan ne a taron manema labarai gabanin kaddamar da taron kasashen da suka amince da wannan yarjejeniyar karo na 22 da zai gudana yau a birnin Marrakesh na kasar Morocco.

A watan Disamban shekarar 2015 ne dai aka amince da yarjejeniyar a birnin Paris na kasar Faransa. Kana a watan Oktoba, kasashe 96 da kungiyar tarayyar Turai (EU) suka sanya hannu a kanta, daga bisani kuma ta fara aiki a ranar 4 ga watan Nuwamban wannan shekara.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China