in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun kubutar da mata da yara 38 daga mayakan Boko Haram
2016-11-02 10:11:28 cri

Hedkwatar tsaron kasar Najeriya ta ce, dakarun kasar sun yi nasarar ceton mata da kananan yara kimanin 38 daga hannun mayakan Boko Haram a jahar Borno dake arewa maso gabshin kasar.

A wata sanarwar da kakakin rundunar sojin Najeriyar Sani Usman ya sanya wa hannu ya ce, sojojin sun kama wasu mayakan na Boko Haram 6, sannan sun jikkata wasu da dama a lokacin da suke musayar wuta da mayakan a kauyen Dumba dake jahar Borno.

Sanarwar ta ce, matan da aka kubutar da su 19 ne, sannan kananan yaran ma 19.

Sanarwar ta kara da cewa, dakarun runduna ta 8 ta musamman ta sojin kasar sun fara gudanar da aikinsu, inda suka lashi takobin tarwatsa maboyar mayakan Boko Haram a yankunan karkara dake jahar Borno a kusa da kan iyakar Najeriya da Nijer.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China