in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara bincike kan hadarin jirgin kasan Kamaru
2016-10-25 10:55:04 cri
Bisa labarin da aka samu daga gidan talabijin na jamhuriyar Kamaru, an ce, an kawo karshen aikin ceto a yankin Eseka dake tsakiyar kasar, bayan hadarin da ya faru ne sakamakon gocewar jirgin kasa daga layinsa a ranar 21 ga wannan wata, kawo yanzu an fara gudanar da bincike game da musabbabin da ya haddasa hadari a hukumance.

Hadarin dai ya haddasa rasuwar mutane 80, yayin da mutane sama da 500 suka jikkata.

Gwamnatin kasar ta ayyana ranar Litinin da ta gabata a matsayin ranar ta'aziya a duk fadin kasar, kuma an sauke rabin tutar kasar domin nuna juyayi ga wadanda suka rasa rayukansu a sanadiyyar hadarin jirgin kasan. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China