in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan wadanda suka rasu sakamakon hadarin jirgin kasan kasar Kamaru ya karu
2016-10-24 19:02:07 cri
Rahotannin baya bayan nan na cewa adadin wadanda suka rasu, sakamakon hadarin jirgin kasar nan da ya auku a kasar Kamaru, ya karu zuwa mutum 79.

An ce a jiya Lahadi, jami'an dake aikin ceto sun fiddo karin wasu gawawwaki daga sassan jirgin da ya sauka daga hanyar sa, kwanaki biyu bayan hadarin da ya auku a tashar Eseka, mai nisan kilomita 120 daga kudu maso yammacin birnin Yaounde fadar mulkin kasar.

Baya ga wadanda suka rasa rayukan su, wasu karin mutanen kimanin 600 na jiyya a asibitoci daban daban, sakamakon hadarin da ya rutsa da su.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China