in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da bincike kan ministan kudin Afirka ta Kudu
2016-10-17 11:06:03 cri
Kwanan baya, babban mai gabatar da kara a kotun kasar Afirka ta Kudu, ya bukaci ministan harkokin kudin kasar Pravin Gordhan, da ya yi bayani game da wani zargi game da cin hanci da karbar rashawa da ake masa nan da ranar 2 ga watan Nuwanba mai zuwa.

Dangane da wannan batu, Pravin Gordhan ya ce, zai tona asirin wasu kudade da aka boye a wasu asusun bankuna, kudaden da suka kai dallar Amurka miliyan dari biyar, wadanda iyalan wani shahararren dan kasuwa mai suna Gupta ya boye, haka kuma wannan iyali yana da dangantaka ta kusa da shugabannin kolin gwamnatin kasar Afirka ta Kudun.

Dangane da wannan lamari, mataimakin shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya nuna goyon bayansa ga aniyar Mr. Gordhan a hukunce a jiya Lahadi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China