in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan Afirka ta Kudu na yunkurin bunkasa sassan ci gaban kasa
2016-10-06 12:20:10 cri
Shugaban Afirka ta Kudu Jacob Zuma, ya ce gwamnatin sa na daukar karin matakai na raya sassan ci gaban kasa, da suka hada da inganta hakar ma'adanai, da noma da samar da ababen more rayuwa, da kuma bunkasa fannin masana'antu, a wani mataki na bada kariya ga sana'o'i, da kuma kara yawan guraben ayyukan yi ga 'yan kasar.

Shugaba Zuma ya bayyana hakan ne a birnin Durban, yayin taron gamayyar kungiyoyin 'yan kwadago na duniya, wanda ya gudana a jiya Laraba. Ya ce taron na bana na gudana a wani lokaci da ake fuskantar tarin matsaloli na tattalin arzikin duniya.

Sai dai duk da haka a cewar sa, muddin Afirka ta Kudu ta samu karin kaso daya bisa dari na ci gaba a shekara mai zuwa kamar yadda aka yi hasashe, hakan zai bada damar samar da guraben ayyukan yi sama da 80,000, yayin da karuwar kaso 3 bisa dari za ta haifar da guraben ayyukan yi 300,000.

Don haka shugaba Zuma ya jaddada kudurin gwamnatin sa na daga matsayin mizanin ci gaban kasar, kamar yadda hakan ke kunshe cikin sabon tsarin bunkasa kasar na shekaru masu zuwa.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China