in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya gana da takwaransa na Banglagesh
2016-10-15 13:17:07 cri
Jiya Jumma'a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaran aikinsa na kasar Banglagesh Abdulla Hammed a babban birnin kasar, Dhaka.

A yayin ganawar tasu, shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin tana godiya matuka dangane da goyon bayan da kasar Banglagesh take bata domin kiyaye muhimman moriyar kasar Sin, haka kuma, tana goyon bayan kasar Banglagesh kan harkokin kiyaye 'yancin kanta da mulkin kasa, sa'an nan, Sin ta amince da kokarin da kasar Banglagesh ta yi wajen tabbatar da zaman lafiya da kuma neman cigaban kasar. Haka zalika, shugaba Xi ya kara da cewa, kamata ya yi kasashen biyu su ci gaba da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu domin aiwatar da ayyukan shirin neman dauwamammen cigaba nan da shekarar 2030 kamar yadda aka tsara, da kuma ciyar da hadin gwiwar kasashe masu tasowa gaba.

A nasa bangaren, shugaba Abdulla Hammed ya ce, kasarsa zata cigaba da nuna goyon baya ga kasar Sin kan harkokin kiyaye muhimman moriyar kasashen biyu, kuma tana son zama abokiyar hadin gwiwar Sin domin neman cigaba tare, kana da karfafa shawarwarin dake tsakanin kasashen biyu kan muhimman harkokin kasa da kasa da shiyya-shiyya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China