in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya bukaci a kara azama wajen bullo da dabarun mulki mai nagarta
2016-10-12 19:56:30 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a fannin gudanarwa, da su bullo da sabbin dabaru na bunkasa sha'anin mulki, ta yadda hakan zai ba da karin kariya ga rayuwar Sinawa.

Shugaban Xi wanda shi ne babban sakataren jam'iyyar kwaminis mai mulkin kasar Sin, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa game da tsarin gudanar da mulki, sanarwar da kuma shugaban hukumar siyasa da shari'a ta kwamitin tsakiyar JKS Meng Jianzhu ya gabatar, yayin wani taron kara wa juna sani na yini biyu, kan harkokin mulki da ya gudana a ranekun Litinin da Talata.

Cikin sanarwar, shugaba Xi ya jaddada muhimmancin gina kasar Sin mai cikakken tsarin tsaro, da kuma managarcin jagoranci. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China