in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nan ba da dadewa kasar Morocco za ta sake dawowa AU
2016-09-14 11:26:16 cri
Majalisar dokokin kasashen Afirka ta bayyana cewa, nan ba da dadewa ba, kasar Morocco za ta sake dawowa cikin kungiyar tarayyar Afirka.

Mai magana da yawun majalisar dokokin kasashen Afirka Roger Nkodo Dang ne ya bayyana hakan a jiya Talata. Ya kuma shaidawa taron manema labarai bayan ganawarsa da takwaransa na majalisar wakilan kasar Morocco Rachid Talbi Alami cewa, majalisar dokokin kasashen Afirka za ta taka rawar da ta dace wajen ganin ta hade kan nahiyar wuri guda. Mr Roger Nkodo ya yaba da shawarar da kasar Moroccon ta yanke na sake dawowa cikin kungiyar ta AU.

Tun a shekarar 1984, lokacin da ake kiran kungiyar da suna, kungiyar hada kan kasashen Afirka ne dai kasar ta Morocco ta fice daga cikin kungiyar. Kana a watan Yuli, Moroccon ta sanar da cewa, za ta sake dawowa cikin kungiyar tarayyar Afirka, shekaru 32 bayan ficewarta daga kungiyar sakamakon wata takaddama da ta shafi kasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China