in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi allah wadai da harin da aka kai a wani sansanin 'yan gudun hijira a Nijer
2016-10-09 13:08:55 cri
Jiya Asabar 8 ga wata, kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU ta yi allah wadai da kakkausar murya kan harin da aka kai a wani sansanin 'yan gudun hijira dake garin Tazalit na yankin Tahoua na kasar Nijer a ranar Alhamis din da ta gabata.

Sa'an nan, a jiya Asabar, kungiyar AU ta fidda wata sanarwa, inda shugabar kungiyar Nkosazana Dlamini Zuma ta yi allah wadai da kakkauwar murya kan wannan mugun harin da aka kai, inda dakaru masu dauke da makamai kimanin guda 40 suka shiga yankin tsaro cikin motoci, tare da kashe sojoji guda 22 wadanda suke kula da tsaron sansanin, yayin da guda uku suka jikkata.

Haka kuma, madam Zuma ta nuna goyon bayan kungiyar AU ga gwamnati da al'ummomin kasar Nijer, tare kuma da nuna juyayi matuka ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, da fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata.

Bugu da kari, ta sake jaddada aniyar kungiyar tarayyar Afirka wajen yaki da dukkan irin 'yan ta'adda da masu tsattsauran ra'ayi a nahiyar Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China