in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi maraba da sako 'yan matan Chibok
2016-10-15 12:22:18 cri
Shugabar kungiyar tarayyar Afrika AU Nkosazana Dlamini-Zuma ta nuna farin ciki game da sako 'yan matan makarantar sakandaren Chibok su 21 daga cikin 'yan matan 276 da mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da su tun a watan Afrilun shekarar 2014 a Najeriya.

Nkosazana Dlamini-Zuma, ta bayyana hakan ne a Lome, babban birnin kasar Togo, a lokacin da take ganawa da kungiyoyin matan Afrika masu ruwa da tsaki a harkokin masana'antu na ruwa, a yayin taron kungiyar tarayyar Afrika kan sha'anin tsaro da ci gaban tekunan Afrika.

An dai saki wasu daga cikin 'yan matan na Chibok ne, bayan shafe sama da shekaru biyu ana garkuwa da su.

Shugabar ta AU ta bukaci al'ummar Najeriya da su tallafawa 'yan matan da aka sako domin komawa hayyacinsu don ci gaba da rayuwa cikin al'umma.

Dlamini-Zuma, ta nuna kyakkyawar fatarta na ganin an sako ragowar 'yan matan nan ba da jimawa ba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China