in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fatan MDD za ta ci gaba da ba da babbar gudummawa a lokacin jagorancin Antonio Guterres,in ji kakakin harkokin wajen Sin
2016-10-15 13:14:20 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a yayin taron maneman labarai cewa, ana fatan MDD za ta ci gaba da ba da babbar gudummawa kan harkokin kiyaye zaman lafiya da tabbatar da ci gaban kasa da kasa da dai sauransu, a lokacin da Antonio Guterres ya dare mukamin babban magatakardan MDD.

Haka kuma, Mr.Geng ya bayyana cewa, kasar Sin ita ce zaunanniyar wakiliya ta kwamitin tsaron MDD, kana, mambar masu daukar alhakin gamayyar kasa da kasa, za ta ci gaba da nuna goyon baya ga ayyukan babban magatakardan MDD yadda ya kamata.

A ranar ga wannan wata ne 13 babban taron MDD karo na 71, ya zartas da kuduri cewa, tsohon firaministan kasar Portugal, kana tsohon babban wakilin MDD dake kula da harkokin 'yan gudun hijira Antonio Guterres ya kasance sabon babban magatakardan MDD a hukumance. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China