in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a kara taimakawa kasashe masu tasowa wajen kara karfin raya kasa
2016-10-07 12:39:02 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wu Haitao, ya yi kira da a kara taimakawa kasashe masu tasowa wajen kara karfin su na raya kasa, da kara nuna goyon baya ga kasashen na Afirka, da kasashe masu karancin ci gaba, da kasashe masu tasowa da ba su kusa da teku, da kuma kananan tsibirai na kasashe masu tasowa.

Kwamiti na biyu na babban taron MDD karo na 71 mai kula da warware matsalolin tattalin arziki ya gudanar da wani taro game da yadda za a gudanar da ayyukansa a jiya Alhamis. A cikin jawabin da ya gabatar wajen taron, Wu Haitao ya bayyana cewa, kamata ya yi a dora muhimmanci ga batun bambancin bunkasuwar kasashe matsakaita, da sa kaimi ga samun bunkasuwa tare, yayin da ake gudanar da ayyukan kwamitin.

Wu Haitao ya bayyana cewa, MDD ta taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da ajandar samun bunkasuwa mai dorewa nan da shekarar 2030, don haka kamata ya yi a tsara buri da shirye-shiryen aiwatar da ayyuka, da dora muhimmanci ga batutuwan kawar da talauci, da tinkarar bala'in dake aukawa halittu, da matsalar sauyin yanayi, da kiwon lafiya da dai sauransu.

Wu Haitao ya kara da cewa, ya kamata kasashe masu ci gaba su cika alkawarinsu na bada gudummawa, yayin da kasashe masu tasowa ya kamata su kara hadin gwiwa da juna, don taimakawa wajen raya hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa da masu wadata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China