in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Antonio Guterres ya zama sabon sakatare janar na MDD
2016-10-14 13:22:18 cri

A jiya Alhamis ne, babban taron MDD ya nada tsohon firaministan kasar Portugal, Antonio Guterres, a matsayin sakatare janar na MDD, inda zai maye gurbin mista Ban Ki-moon wanda wa'adin aikinsa zai kare a wannan shekara.

Mambobin babban taron MDD 193 ne suka amince da kudurin nadin nasa, bayan da jakadan kasar Rasha dake MDD, Vitali Tchourkine kana shugaban kwamitin sulhu na MDD na watan Oktoba, ya sanar da taron MDD wannan shawarar bayan da ya samu goyon bayan kwamitin game da nadin mista Guterres.

A ranar ga watan Janairun shekarar 2017 ne zai fara wa'adin aikinsa na shekaru biyar, kuma wa'adin zai kare a ranar 31 ga watan Disamban shekarar 2021. Cikakken dan siyasa mai shekaru 67 da haifuwa, mista Guterres ya rike mukamin babban kwamishinan hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD daga watan Yunin shekarar 2005 zuwa watan Disamban shekarar 2015. Kafin ya rike shugaban hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, mista Guterres ya kwashe tsawon shekaru 20 yana aiki a gwamnatin kasar. Ya kuma zama faraministan Portugal daga shekarar 1995 zuwa shekarar 2002. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China