in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a daga matsayin karfin bunkasuwar kasashen Afirka
2016-10-11 13:32:08 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi, ya yi kira ga kasa da kasa da su maida hankali ga inganta karfin samun bunkasuwar kasashen dake nahiyar Afirka, su kuma sa lura ga bukatun kasashen Afirka, na zamanintar da aikin gona, da masana'antu, da ayyukan more rayuwa da dai sauransu.

Bikin makon Afirka ya gudana a wannan rana a cibiyar MDD, bikin da aka yiwa lakabi da "kara raya dangantakar abokantaka ta samun bunkasuwa mai dorewa, da gudanar da ayyukan siyasa mai dacewa da wanzar da zaman lafiya a nahiyar Afirka".

A gun bikin bude taron, Mr. Liu Jieyi ya gabatar da jawabi, wanda a cikin sa ya bayyana cewa, kamata ya yi a aiwatar da ajendar samun bunkasuwa mai dorewa ta shekarar 2030, da ajendar shekarar 2063 ta nahiyar Afirka, a kuma maida hankali ga cimma burin kawar da talauci da yunwa, da kara hadin gwiwa a fannin samar da kayyayaki a yankin, da sa kaimi ga samun bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'umma, da kiyaye muhalli a nahiyar Afirka.

Ya ce, ya kamata a tsaya tsayin daka kan ka'idar aiwatar da mnufofi masu dacewa da ra'ayoyin kasashen nahiyar, da nuna goyon baya ga kasashen ta, ta yadda za su tsara manufofin samun bunkasuwa da za su dace da yanayinsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China