in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi taron dandalin tattaunawar zuba jari a Afirka karo na biyu a birnin Guangzhou
2016-08-29 16:46:30 cri
Za a kira taron dandalin tattaunawar zuba jari a nahiyar Afirka a birnin Guangzhou na kasar Sin tun daga ranar 7 zuwa 8 ga watan Satumba mai zuwa, inda shugabannin gwamnatocin kasashen Afirka sama da 30, da wasu jakadun kasashen Afirka dake nan kasar Sin, da kuma wasu wakilan kamfanoni masu zaman kansu za su halarci wannan taro. Haka kuma, wakilan bankin duniya, hukumar raya masana'antu ta MDD, hukumar raya kasashe ta MDD, hukumar kula da tattalin arzikin Afirka ta MDD, asusun raya harkokin noma na kasa da kasa da dai sauran kungiyoyin kasa da kasa da na shiyya-shiyya za su halarci taron, a bangaren kasar Sin kuma, wasu shugabannin gwamnatin kasar, da wakilan kamfanonin kasar da abin ya shafa za su halarci taron, inda gaba daya kimanin mahalarta dari uku za su halarci taro.

Gwamnatin lardin Guangdong, bankin raya kasa na kasar Sin da kuma bankin duniya ne suka shirya wannan taro cikin hadin gwiwa, bisa taken "yin musayar fasahohin neman bunkasuwa, domin inganta hadin gwiwar Sin da Afirka", haka kuma, a yayin taron manema labarai da aka kira a jiya Litinin dangane da wannan taro, mataimakin babban sakataren gwamnatin lardin Guangdong Zhang Aijun ya bayyana cewa, yanzu, an tabbatar da cewa,ministocin kasashen Afirka sama da 20 ne za su halarci taron, kuma an shirya tsaf don gudanar da wannan taron cikin nasara.

Hadin gwiwar tattalin arziki dake tsakanin lardin Guangdong da kasashen Afirka tana bunkasa cikin sauri, musamman ma a tsakanin shekarar 2003 zuwa shekarar 2015, darajar cinikayya dake tsakanin lardin Guangzhou da Afirka ta karu daga dallar Amurka biliyan 2.8 zuwa dallar Amurka biliyan 43.1, adadin da ya ninka har sau 14. A halin yanzu kuma, nahiyar Afirka ta kasance daya daga cikin manyan abokan cinikayya guda 10 na lardin Guangdong. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China