in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu ba da shawara kan harkokin watsa labarai na Sin da Afirka sun mai da hankali kan tattara jari da hikima tsakanin Sin da Afirka
2016-08-13 13:48:33 cri
A jiya Jumma'a 12 ga wata, taron karawa juna sani tsakanin masu ba da shawara kan harkokin watsa labarai na Sin da na kasashen Afirka ya gudana a birnin Mombasa na kasar Kenya, inda masu ba da shawara da wakilan kafofin yada labarai da masana da wakilan sassan siyasa da na masana'antu sama da 150 da suka fito daga Sin, da Kenya, da Afirka ta Kudu, da Senegal, da Tanzaniya da dai sauransu sama da 20 suka halarci wannan dandalin tattaunawa, domin yin shawarwari kan harkokin hadin gwiwa da samun ci gaba tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Shugaban kungiyar kula da harkokin diplomasiya ta Sin, Li Zhaoxing ya bayyana a gun dandalin tattaunawar cewa, an sami babbar nasara a gun taron koli na Johannesburg na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka gudanar a watan Disamban bara. Bisa alkaluman da aka bayar, an ce, kawo yanzu baki daya yawan yarjeniyoyin da aka daddale ya kai sama da 240, yayin da jimillarsu ta kai sama da dala biliyan 50.

Wakilai daga sassan siyasa da masana'antu da na kafofin yada labarai da yawa dake halartar taron sun bayyana cewa, yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka ba ma kawai na bukatar tattara jari ba, har ma ana bukatar tattara hikima.

Shugaban kwalejin nazarin harkokin watsa labarai na jami'ar Renmin ta Sin, kana tsohon darektan ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwa, Zhao Qizheng ya ba da shawara cewa, kamata ya yi kafofin yada labarai na Sin da na kasashen Afirka su yi amfani da wannan zarafi na yin hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, su sami ci gaba tare, su sami moriyar tare, kuma su dora muhimmanci kan watsa labarai daga dukkan fannoni a yayin da ake yada fasahohin da Sin da kasashen Afirka suka samu daga wajen junansu.

Ministan sufuri da manyan ayyuka na Kenya, James Macharia ya gabatar da jerin ayyukan da ake yi da kuma za a yi bisa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, kamar hanyar jirgin kasa da ta hada Mombasa da Nairobi da sauransu. Ya ce, ana yin hakikanin hadin gwiwa tsakanin Sin da Kenya bisa bukatun gaggawa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China