in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afirka, Sin da Amurka za su tattauna batun tsaron teku
2016-07-27 19:28:37 cri
Ana saran tattaunawar da kasashen Afirka, Sin da Amurka za su yi a wannan shekara za ta mayar da hankali kan tsaron teku da albarkatun ruwa, maimakon batutuwan tsaro kadai da taron ya saba tattaunawa a shekarar 2014.

Darektan kula da harkokin siyasa a ma'aikatar harkokin wajen kasar Togo Dr. Bakayota Koffi Kpaye shi ne ya bayyana hakan a jiya Talata yayin da yake zantawa da kamfanin dillancin labaru na Xinhua na kasar Sin.

A yau Laraba da kuma gobe Alhamis za a fara tattauna a Lome kamar yadda cibiyar Cater ta tsara, gabanin taron kolin kungiyar tarayyar Afirka kan tsaro da ci gaban harkokin teku a Afirka da za a gudanar a watan Oktoba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China