in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban Sin ya gana da shugabannin tawagar wakilan bangaren Afirka a taron aiwatar da sakamakon taron FOCAC na Johannesburg
2016-07-28 19:18:46 cri
A yau Alhamis ne, a nan birnin Beijing, mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya gana da shugabannin tawagar wakilan bangaren Afirka wadanda suke kula da ayyukan aiwatar da sakamakon dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka watau FOCAC da aka yi a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu.

A yayin ganawar tasu a na birnin Beijing, Li Yuanchao ya ce, an cimma nasarar taron FOCAC da ya gudana a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu a shekarar da ta gabata, inda aka bude wani sabon babin hadin gwiwar Sin da Afirka iri na cimma moriyar juna da kuma neman bunkasuwa cikin hadin gwiwa.

A saboda haka, ya ce ana fatan Sin da Afirka za su karfafa fahimtar juna dake tsakaninsu, haka kuma za su ci gaba da inganta hadin gwiwarsu yadda ya kamata, a yayin da ake aiwatar da sakamakon taron na FOCAC. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China