in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na MDD ya yi kira da a mai da hankali kan yanayin jin kai a Syria
2016-08-19 10:59:16 cri
A jiya Alhamis 18 ga wata, manzon musamman na babban sakataren MDD kan batun Syria, mista Staffan de Mistura ya yi kira ga kasashen duniya da su mai da hankali kan yanayin jin kai da ake ciki a kasar Syria, inda ya kalubalanci bangarori daban daban dake musayar wuta da su tsagaita bude wuta na a kalla sa'o'i 48, ta yadda za a hanzarta jigilar kayayyakin agaji ga wuraren da ke bukata.

A wannan rana, mista Staffan de Mistura ya soke taron mako-mako na rukunin shigar da kayayakin jin kai cikin Syria a Geneva, da zummar jawo hankulan kasa da kasa kan yanayin da ake ciki a fannin jin kai a Syria, musamman ma a yankin Aleppo, wanda yake kara tsananta a kullum.

A ranar Talata ne, kwamitin cika aiki na kasa da kasa mai zaman kansa kan batun Syria da hukumar kula da hakkin bil'adam ta MDD ta dora alhaki ya bayyana cewa, a cikin makwannin da suka wuce, bangarorin da ke fada da juna a Syria sun sake gwabzawa a yankin Aleppo, lamarin da ya jefa fararen hula kimanin miliyan 2 cikin matsalar karancin abinci da ruwan sha.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China