Rahotanni na cewa, bam na farko ya fashe ne a dab da wani sansanin dakarun Kurdawa, maharan sun kai hare-haren ta hanyar tuka wata mota shake da abubuwan fashewa a cikinta, kana bam na biyu kuma ya fashe ne a shingen duba ababan hawa na dakarun Kurdawa. Mutane da dama sun ji munanan raunuka, watakila yawan mutanen da suka mutu a sakamakon harin zai karu. Yanzu haka ana ci gaba da aikin nema da bada ceto ga mutanen da suka ji rauni.
Kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai harin. (Zainab)