in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kafa sabuwar majalisar ministoci a kasar Syria
2016-06-23 11:16:46 cri
Shugaban kasar Syria Bashar al Assad ya bada umurni a jiya ranar 22 ga wata, inda ya ba wa ministan wutar lantarki na kasar Imad Hammis ikon kafa sabuwar majalisar ministoci ta kasar.

Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na kasar Syria ya bayar, an ce, za a nada Hammis a matsayin sabon firaministan kasar, don ya maye gurbin firaministan kasar mai ci yanzu Wael Nader al-Halqi. Ana kuma sa ran ba da jimawa ba za a gabatar da jerin sunayen sabbin ministoci.

Hammis ya zama ministan wutar lantarki na kasar a cikin gwamnatin al-Halqi.

An yi zaben majalisar dokokin jama'ar kasar Syria a ranar 13 ga watan Afrilu na bana. Sabuwar majalisar dokokin ta yi rantsuwar kama aiki a ranar 6 ga watan Yuni. Bisa dokokin kasar, ya kamata a kafa sabuwar majalisar ministocin kasar a cikin kwanaki 40 bayan rantsuwar kama aikin sabuwar majalisar dokokin kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China