in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An janye wasu mazauna birnin Aleppo na Syria daga yankin dake cikin hannun dakarun jam'iyyar adawa na kasar
2016-07-31 13:10:24 cri
Jiya Asabar, bisa kiran da gwamnatin kasar Syria ta yi musu, wasu mazauna birnin Aleppo dake arewacin kasar Syria sun fita daga yankin dake cikin hannun dakarun jam'iyyun adawa da gwamnatin kasar.

Rahotanni sun ce, wasu dakaru sun taba hana wadannan fararen hula ficewa daga yankin dake karkashin ikonsu, a daya bangare kuma, wasu dakaru sun mika wuya ga gwamnatin kasar.

A baya, gwamnatin kasar Syria ta bude manyan hanyoyi guda uku ga al'ummomin kasar domin janye su daga yankin dake karkashin mallakar dakaru na jam'iyyun adawa, haka kuma, gwamnatin ta yi alkawarin cewa, za ta kula da al'ummomin yadda ya kamata bayan sun fita daga yankin.

Birnin Aleppo ya taba kasance cibiyar tattalin arzikin kasar Syria, yayin da kuma birni mafi girma na wannan kasa. Amma, cikin dogon lokacin da suka gabata, sojojin gwamnatin kasar suna mallakar yammacin birnin, yayin da gabashin birnin ke karkashin mallakar dakaru na jam'iyyun adawa da kuma kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi.

Kana, a halin yanzu, sojojin gwamnatin kasar suna yin kawanya kan yankin dake karkashin mallakar dakarun, inda sojojin gwamnatin suka yi kira ga dakarun jam'iyyun adawa da su aje makamansu don mika wuya.

Kaza kila, shugaban kasar Syria Bashar al Assad ya samar da wani shirin nuna afuwa a ran 28 ga watan nan da muke ciki, inda ya sanar da yin afuwa ga dakarun da suka mika wuya ga gwamnati cikin watanni uku masu zuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China