in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birtaniya ba za ta fara ayyukan ficewarta daga EU ba kafin karshen bana
2016-08-16 10:07:52 cri
Kakakin fadar firaministan kasar Birtaniya ya bayyana a jiya Litinin cewa, kafin karshen shekarar bana, kasar Birtaniya ba za ta fara ayyukan dake shafar ficewarta daga kungiyar tarayyar kasashen Turai, wato EU ba, a halin yanzu kuma, firaministar kasar Theresa May tana dukufa wajen kulla wata yarjejeniya da kungiyar EU, wadda za ta dace da moriyar kasarta.

Haka kuma, bisa labarin da jaridar Sunday Times ta kasar Birtaniya ta samar, an ce, hukumar dake kula da harkokin ficewar kasar daga kungiyar EU da harkokin diflomasiyya ba ta sami isassun ma'aikata ba, shi ya sa, mai iyuwa, kasar Burtaniya za ta jinkirta lokacin fara gudanar da ayyukan ficewarta daga kungiyar EU zuwa karshen shekarar 2017.

Dangane da wannan harka, kakakin fadar firaministan kasar Birtaniya ya ce, aikin ficewar kasar daga kungiyar EU wani muhimmin aiki ne mai nauyi kuma na dogon lokaci, shi ya sa, ba za a fara wannan aiki ba a hukunce kafin karshen shekarar bana, amma kakakin bai bayyana ko yaushe za a fara gudanar da ayyukan da abin ya shafa ba.

Bisa dokokin kungiyar EU da abin ya shafa, ya kamata mambar dake son fice daga kungiyar ta bi kuduri mai lamba 50 na yarjejeniyar Lisbon, sa'an nan ta fara ayyukan ficetarta daga kungiyar EU, amma wannan aiki na dogon lokaci ne, a kalla za a kashe shekaru biyu wajen kammala ayyukan da abin ya shafa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China