in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birtaniya za ta ci gaba da neman kafa dangantaka mai karfi tsakaninta da Sin
2016-08-02 10:19:03 cri
Bisa labarin da kafofin yada labarai na Birtaniya suka bayar, an ce, bayan da gwamnatin kasar ta yanke shawarar wucin gadi ta jinkirta dora niyya kan aikin samar da wutar lantarki bisa makamashin nukiliya na Hinkley Point, a jiya Litinin, daya ga wata, kakakin firaministar kasar Birtaniya madam Theresa Mary May ta bayyana cewa, kasar za ta ci gaba da neman kafa dangantaka mai karfi tsakaninta da kasar Sin.

Kafofin yada labarai sun yi amfani da maganar kakakin madam Theresa Mary May cewa, sabuwar gwamnatin kasar na fatan yin nazari kan aikin Hinkley Point cikin taka-tsantsan. Birtaniya na dora muhimmanci kan dangantaka tsakaninta da Sin. Ta ce, Sin na taka muhimmiyar rawa a harkokin duniya, da tattalin arzikin duniya, da kuma jerin batutuwan duniya, shi ya sa kasar za ta kokarta kafa dangantaka mai karfi tsakaninsu.

A sa'i daya, kakaki ba ta yi tsokaci ba cewa, ko ana sake yin la'akari da aikin Hinkley Point sabo da tsaron kasa. Ta furta cewa, kasar Birtaniya tana ci gaba da bude kofa ga kamfanoni, da zummar samun jari da za a zuba a kasar daga ketare. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China