in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na Sin ya gana da ministocin wajen kasashen Afirka 4
2016-07-29 09:25:45 cri
A jiya Alhamis 28 ga wata ne ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya gana da ministocin wajen kasashen Mali mista Abdoulaye Diop, da ta Madagascar madam Béatrice Atallah, da na Comoros mista Mohamed Bacar Dossar, da na Kongo Kinshasa, mista Raymond Tshibanda Tunga Mulongo a nan birnin Beijing. Ministocin dai na halartar taron masu shiga tsakani ne, game da sakamakon da aka samu a gun taron koli na Johannesburg, na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Wang Yi ya bayyana cewa, bisa wannan taro na masu shiga tsakani da za a gudanar, Sin na fatan bayyana alama a fili ga duniya cewa, ko da yake ana fuskantar matsalar rashin samun ci gaban tattalin arziki a duniya, duk da hakan Sin za ta cika alkawarin da ta dauka. Kaza lika ana cikin yanayi mai kyau game da hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, kuma za a sami makoma mai kyau a wannan fanni.

A nasu bangare, ministocin kasashen Afirkan sun bayyana cewa, kasashen nahiyar za su yi amfani da wannan zarafi, wajen tabbatar da sakamakon da aka samu a taron kolin Johannesburg, domin gudanar da shawarwari tare da kasar Sin kan batun hadin gwiwa, da neman samun ci gaba tare, da kara hada kai waje guda, ta yadda za su kara amincewa da nuna wa juna goyon baya, kan batutuwan da suka shafi babbar moriyar juna, da ma sauran harkokin da suka fi jawo hankulan bangarorin biyu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China