in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da taron masu shiga tsakani kan sakamakon taron koli na  Johannesburg na dandalin FOCAC a Beijing
2016-07-20 16:05:11 cri
A yau Laraba ce, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin, Lu Kang ya bayyana cewa, bisa shawarwarin da aka cimma tsakanin Sin da kasashen Afirka, za a gudanar da taron masu shiga tsakani game da sakamakon da aka cimma a yayin taron koli na Johannesburg na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka wato FOCAC a Beijing a ranar 29 ga wata, inda shugabannin majalisar gudanarwar Sin za su halarci bikin bude taron tare da yin jawabai.

Lu Kang ya ce, masu shiga tsakani kan sakamakon da aka cimma a gun taron kolin Johannesburg na kasashen Afirka 52, da jakadun kasashen Afirka a Sin, da wakilan kamfanonin kwamitin kula da ci gaban dandalin FOCAC da sauransu za su halarci wannan taro. Dadin dadawa, za a kira taron shawarwari tsakanin shugabannin hukumomin hada hadar kudi na Sin da mahalarta taron daga kasashen Afirka, da taron musayar ra'ayi kan hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki da cinikayya tsakanin bagarorin biyu, da bikin rattaba hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwa da sauransu.

Lu Kang ya bayyana cewa, makasudin shirya wannan taro shi ne musayar ra'ayi kan sakamakon da aka samu ta hanyar yin hadin gwiwa, da yin mu'amala kan yin hadin gwiwa, da kara sa kaimi ga tabbatar da sakamakon da aka samu a gun taron kolin Johannesburg, ta yadda za a kara zurfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka domin samun ci gaba tare.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China