in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin zata kafa wasu masana'antunta a kasar Senegal
2015-12-07 10:43:54 cri
Kasar Sin zata kafa wasu masana'antunta a kasar Senegal tare da bude babban yankin masana'antu na nan gaba kusa da birnin Dakar, hedkwatar kasar Senegal, in ji shugaban kasar Senegal Macky Sall a ranar Asabar a yayin kammala dandalin Sin da Afrika (FOCAC) a Johannesburg na kasar Afrika ta Kudu.

Yankin masana'antun za a gina shi a cibiyar birnin Diamniadio mai tazarar kilomita 30 daga birnin Dakar, bisa shirin gyare gyaren birane da ya kunshi gina unguwannin hukumomi, yankunan gidajen jama'a, yankunan masana'antu, jami'o'i da kuma filayen hada hada. A cewar Shugaba Macky Sall, kasar Sin na aiki domin taimakawa Afrika kasancewa cikin cigaban masana'antu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China