in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron koli na Johannesburg na Dandalin FOCAC na da alfanu sosai in ji shugaban Guinea-Bissau
2015-12-10 13:17:00 cri
Shugaban kasar Guinea-Bissau, Jose Mario Vaz, ya nuna jinjina ga taron koli na Johannesburg na dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afrika na FOCAC, wanda ya kimanta da wani abin da ke tattare da alfanu ga makomar cigaban tattalin arzikin Afrika.

Kasar Sin a shirye take kana kofarta a bude take wajen raba kwarewarta tare na nahiyar Afrika a fannin samun bunkasuwa, in ji mista Jose Mario Vaz a gaban manema labarai bayan ya koma kasarsa a ranar Laraba. Shugaban Guinea-Bissau ya jaddada cewa, dangantakar Sin da Afrika, dangantaka ce mai muhimmanci bisa ta manyan tsare tsare,wadda ke iya jurewa kalubale na rashin cigaba. A cewar shugaba Jose Mario Vaz, hadin kai a tsakanin Afirka da kasar Sin zai dore, wato za a cigaba da samar da karin moriyar juna. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China