Haka kuma, ya ce, wasu dakaru sun shiga wani wurin Ibadan 'yan shi'a da safiyar wannan rana, inda dakaru guda biyu suka tayar da boma-boman da ke jikinsu, yayin da ragowar maharani kuma suka kama wasu mutanen da suke aikin ziyara.
Rahotanni na cewa, an yi musayar wuta tsakanin jami'an tsaron Iraki da maharani, inda aka halaka dukkan maharani kana aka ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.
Jami'in ya kuma bayyana cewa, fashewar da kuma musayar wuta tsakanin sassan biyu, sun haddasa mutuwar mutane a kalla 20 yayin da wasu 70 suka jikkata. Da alamun kungiyar IS ce ta shirya da kuma aiwatar da wannan hari, in ji shi.
Amma ya zuwa yanzu, babu wani mutum ko wata kungiya da ta sanar da daukar alhakin kai wannan hari. (Maryam)