in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Iraqi ta bukaci kasashen duniya da su yi tofin Alla-tsine kan sojojin Turkiyya dake kasar
2015-12-11 10:42:57 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Iraqi ta ba da wata sanarwa, inda ta bayyana cewa, kasar Iraqi ta riga ta tuntubi M.D.D. da kungiyar kawancen kasashen Larabawa AL da ma sauran kungiyoyin kasa da kasa, don yin kira ga kasashen duniya da su goyi bayan matsayinta, na yin Allah-wadai da kasancewar sojojin Turkiyya a kasar. A wannan rana, a birnin Ankara shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya jaddada cewa, Turkiyya ba za ta janye sojojinta daga yankin arewacin kasar Iraqi ba.

Rahotanni na cewa Iraqi ta bukaci mambobin kasashe 5 dake da kujerun din-din-din a M.D.D. da sauran kasashen duniya da dama, da su tsaya matsayi guda, na yin alla-wadai da Turkiyya. A sa'i daya kuma, Iraqi ta bukaci kungiyar AL da ta shirya taron ministocin harkokin kasashen wajen kungiyar don tattauna wannan batu, tun bayan da Turkiyya ta yi shisshigi a yankin kasar Iraqi, ta yadda za cimma ra'ayi guda game da wannan kutse da Turkiya ta yi cikin kasashen Larabawa.

A yayin wani taron manema labarai da shugaban Turkiyya Erdogan ya yi, tare da shugaban Bosnia-Herzegovina Dragan Covic da ya kai ziyara a kasar, ya ce, sojojin Turkiyya da ke birnin Mosul sojoji ne da ke samar da horo, sabo da haka, ba za su janye su daga kasar Iraqi ba. Erdogan ya ce, Turkiyya ta jibge sojojinta a yankin arewacin kasar Iraqi ne domin biyan bukatun da gwamnan jihar Mosul ya gabatar. Tun daga shekarar 2014 ne, Turkiyya ta fara horar da sojojin Kurdawa a kasar Iraqi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China